Buhari ya ce ba tallafin gwamnati aka wawushe a jihohi ba
Fadar shugaban Najeriya ta ce ba tallafin gwamnati aka wawushe a jihohi ba, sabanin yadda wasu ke zargin gwamnatocin jihohi da ƙin raba kayayyakin. Gwamnatin Najeriya ta ce tallafin da aka wawushe na wasu ƴan kasuwa ne da suka tara domin agaza wa mutane. Mai magana da yawun shugaban Najeriya Malam Garba Shehu ya shaida wa BBC cewa kayan abincin da mutane suka wawushe a jihohi ba na Gwamnatin Tarayya ba ne. "Na ƴan kasuwa ne da suka tara kudi don taimakawa kan wahalar da annobar korona ta jefa mutane," in ji shi. Jihohi da dama ne aka ɓalle wuraren ajiye abinci kuma aka wawushe su. Jihohin Adamawa da Kaduna da Filato da Taraba da Abuja da Cross River da Kwara da Oyo na cikin jihohin da suka fuskanci ayyukan matasan. Wasu da dama a Najeriya sun yi zargin gwamnatocin jihohi da jinkirta raba kayan agaji, wanda ya kawo wannan gaba da wasu da ake zargin ɓata-gari ne suka ɓalla wuraren ajiyar suna kwashewa. Amma wata sanarwar da jami`in yaɗa labaran ƙungiyar gwamnonin Najeriyar, Abd...
Comments
Post a Comment