Fadar shugaban Najeriya ta ce ba tallafin gwamnati aka wawushe a jihohi ba, sabanin yadda wasu ke zargin gwamnatocin jihohi da ƙin raba kayayyakin. Gwamnatin Najeriya ta ce tallafin da aka wawushe na wasu ƴan kasuwa ne da suka tara domin agaza wa mutane. Mai magana da yawun shugaban Najeriya Malam Garba Shehu ya shaida wa BBC cewa kayan abincin da mutane suka wawushe a jihohi ba na Gwamnatin Tarayya ba ne. "Na ƴan kasuwa ne da suka tara kudi don taimakawa kan wahalar da annobar korona ta jefa mutane," in ji shi. Jihohi da dama ne aka ɓalle wuraren ajiye abinci kuma aka wawushe su. Jihohin Adamawa da Kaduna da Filato da Taraba da Abuja da Cross River da Kwara da Oyo na cikin jihohin da suka fuskanci ayyukan matasan. Wasu da dama a Najeriya sun yi zargin gwamnatocin jihohi da jinkirta raba kayan agaji, wanda ya kawo wannan gaba da wasu da ake zargin ɓata-gari ne suka ɓalla wuraren ajiyar suna kwashewa. Amma wata sanarwar da jami`in yaɗa labaran ƙungiyar gwamnonin Najeriyar, Abd...
Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya karbi bakuncin gwamnan jihar Zamfara Matawalle ya ce rusa rundunar SARS matsala ne ga al'ummar jiharsa - Ya bukaci a kara tura jami'an tsaro jihar domin kawar da yan bindiga Gwamnan jihar Zamfara, Bello Muhammad Matawalle, a ranar Juma'a ya bayyana cewa sama da yan kasar waje 31 aka kora daga Najeriya saboda hakan ma'adinai ba bisa doka ba a jihar. Gwamna ya kara da cewa mutane 20 yan bindiga suka kashe ranar Laraba bayan rusa rundunar SARS da gwamnatin tarayya tayi, kisan-mutane-20-matawalle-ya-kaiwa-buhari-kuka-villa-hotuna. Gwamnat Matawalle ya bayyana hakan ne ga manema labaran fadar shugaban kasa bayan ganawa da shugaba Muhammadu Buhari inda ya bukaci a dawo masa da jami'an SARS. Ya kawo wa shugaba Buhari ziyara ne kan lamarin tsaron jihar. "Na zo ne domin bayyanawa shugaban kasa halin da jihar ke ciki. Bayan rusa rundunar SARS mun fuskanci wasu matsaloli, musamman shekaran jiya (Laraba) inda aka kashe mutane 20 a kar...
Wannan satin ya kasance mai matukar tarihi a kasar Najeriya gaba daya - Masu zanga-zangar EndSARs sun zarce da kashe-kashe tare da kone-kone wanda ya koma tarzoma - Adesina ya ce ko nan gaba Najeriya ta tarwatse, toh babu shakka kiyayya ce ta tarwatsa ta Wannan mako ne mai cike da tarihi a kasar nan. A cikin watan nan ne Najeriya ta cika shekaru 60 da samun 'yancin kai kuma shugaban kasa Muhammadu Buhari ya horemu da mu zauna lafiya tare da hada kai da kuma mantawa da tsohuwar gaba wacce ke kawo rikici. Abinda ya fara tamkar zanga -zangar lumana daga wasu matasan Najeriya a kan cin zarafin da rundunar ta musamman ta yaki da fashi da makami ke yi a Najeriya, ya koma wani abu na daban da ya kawo kashe-kashe da rikici. Tunanina da ta'aziyyata ga iyalan wadanda suka rasa rayukansu. -idan-najeriya-ta-tarwatse-kiyayya-ce-ta-tarwatsa-ta---femi-adesina Wasu jama'a suna alakanta hakan da kuskuren 1914 wanda aka hada yankin arewaci da kudanci har aka samu Najeriya. Tun daga nan ala...
Comments
Post a Comment