Fadar shugaban Najeriya ta ce ba tallafin gwamnati aka wawushe a jihohi ba, sabanin yadda wasu ke zargin gwamnatocin jihohi da ƙin raba kayayyakin. Gwamnatin Najeriya ta ce tallafin da aka wawushe na wasu ƴan kasuwa ne da suka tara domin agaza wa mutane. Mai magana da yawun shugaban Najeriya Malam Garba Shehu ya shaida wa BBC cewa kayan abincin da mutane suka wawushe a jihohi ba na Gwamnatin Tarayya ba ne. "Na ƴan kasuwa ne da suka tara kudi don taimakawa kan wahalar da annobar korona ta jefa mutane," in ji shi. Jihohi da dama ne aka ɓalle wuraren ajiye abinci kuma aka wawushe su. Jihohin Adamawa da Kaduna da Filato da Taraba da Abuja da Cross River da Kwara da Oyo na cikin jihohin da suka fuskanci ayyukan matasan. Wasu da dama a Najeriya sun yi zargin gwamnatocin jihohi da jinkirta raba kayan agaji, wanda ya kawo wannan gaba da wasu da ake zargin ɓata-gari ne suka ɓalla wuraren ajiyar suna kwashewa. Amma wata sanarwar da jami`in yaɗa labaran ƙungiyar gwamnonin Najeriyar, Abd...
HANYAR DA ZA’A BI DOMIN A INGANTA TSARON CIKIN GIDA NIGERIA Daga Alkalamin Malam Datti Assalafiy A cikin kowace kasa a duniya, ‘yan sanda sune suke da alhakkin tabbatar da tsaro na cikin gida, idan bukata ta kama suna taba aikin soja, babu Kasar da ta zauna lafiya face sai da ta gyara ‘yan sandan ta Amma a Kasarmu Nigeria me yasa aka dakatar da diban sabbin ‘yan sanda masu mukamin Constable? Yanzu muna cikin shekara na biyu da aka dakatar da diban sabbin ‘yan sandan Nigeria masu mukamin Constable, sakamakon rashin jituwa da aka samu tsakanin Maigirma tsohon shugaban rundinar ‘yan sandan Nigeria IGP Muhammad Abubakar Adamu (rtd), da kuma shugaban hukumar kula da aikin ‘yan sanda na kasa (Chairman Police Service Commission) akan batun diban sabbin ‘yan sanda masu mukamin Constable Maigirma tsohon shugaban ‘yan sanda IGP Muhammad Abubakar Adamu yace shi yake da ikon diban sabbin kuratan ‘yan sanda bisa dokar aikin ‘yan sanda, Chairman Police Service Commission sunce su ke da ikon diban k...
Ana tsakiyan Ibada, bata gari cikin al'umma sun yi aika-aika - Masu garkuwa da mutanen sun bukaci kudin fansa milyan hamsin, amma daga baya sun rage - Har yanzu ba'a samu ceto wadanda aka sace daga hannunsu ba Wasu yan bindiga da ake kyautata zaton masu garkuwa da mutane ne sun kai hari Masallaci kuma sun sace mutane 17 a unguwar Gwargwada-Sabo dake garin Gadabuke a jihar Nasarawa. An tattaro cewa wadanda aka sace sun hada da wani ma'aikacin jami'ar Ahmadu Bello Zariya, mata 3 a wasu maza 13, a cewar rahoton Daily Trust. Wani mazaunin unguwar mai suna Usman ya ce wannan abu ya faru ne daren Talata yayinda ake Sallan Isha'i. "Yan bindigan na shigowa suka fara harbin kan mai uwa da wabi, yayinda sauran suka shiga cikin Masallacin sukayi awon gaba da su cikin daji," yace. Limamin Masallacin da yaranshi kadai suka tsira.Iyalan wadanda aka sace sun samu tattaunawa da masu garkuwa da mutanen kuma sun bukaci milyan daya-daya kan kowani mutum. "Da farko sun b...
Comments
Post a Comment