HANYAR DA ZA’A BI DOMIN A INGANTA TSARON CIKIN GIDA NIGERIA Daga Alkalamin Malam Datti Assalafiy A cikin kowace kasa a duniya, ‘yan sanda sune suke da alhakkin tabbatar da tsaro na cikin gida, idan bukata ta kama suna taba aikin soja, babu Kasar da ta zauna lafiya face sai da ta gyara ‘yan sandan ta Amma a Kasarmu Nigeria me yasa aka dakatar da diban sabbin ‘yan sanda masu mukamin Constable? Yanzu muna cikin shekara na biyu da aka dakatar da diban sabbin ‘yan sandan Nigeria masu mukamin Constable, sakamakon rashin jituwa da aka samu tsakanin Maigirma tsohon shugaban rundinar ‘yan sandan Nigeria IGP Muhammad Abubakar Adamu (rtd), da kuma shugaban hukumar kula da aikin ‘yan sanda na kasa (Chairman Police Service Commission) akan batun diban sabbin ‘yan sanda masu mukamin Constable Maigirma tsohon shugaban ‘yan sanda IGP Muhammad Abubakar Adamu yace shi yake da ikon diban sabbin kuratan ‘yan sanda bisa dokar aikin ‘yan sanda, Chairman Police Service Commission sunce su ke da ikon diban k...
Fadar shugaban Najeriya ta ce ba tallafin gwamnati aka wawushe a jihohi ba, sabanin yadda wasu ke zargin gwamnatocin jihohi da ƙin raba kayayyakin. Gwamnatin Najeriya ta ce tallafin da aka wawushe na wasu ƴan kasuwa ne da suka tara domin agaza wa mutane. Mai magana da yawun shugaban Najeriya Malam Garba Shehu ya shaida wa BBC cewa kayan abincin da mutane suka wawushe a jihohi ba na Gwamnatin Tarayya ba ne. "Na ƴan kasuwa ne da suka tara kudi don taimakawa kan wahalar da annobar korona ta jefa mutane," in ji shi. Jihohi da dama ne aka ɓalle wuraren ajiye abinci kuma aka wawushe su. Jihohin Adamawa da Kaduna da Filato da Taraba da Abuja da Cross River da Kwara da Oyo na cikin jihohin da suka fuskanci ayyukan matasan. Wasu da dama a Najeriya sun yi zargin gwamnatocin jihohi da jinkirta raba kayan agaji, wanda ya kawo wannan gaba da wasu da ake zargin ɓata-gari ne suka ɓalla wuraren ajiyar suna kwashewa. Amma wata sanarwar da jami`in yaɗa labaran ƙungiyar gwamnonin Najeriyar, Abd...
Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya karbi bakuncin gwamnan jihar Zamfara Matawalle ya ce rusa rundunar SARS matsala ne ga al'ummar jiharsa - Ya bukaci a kara tura jami'an tsaro jihar domin kawar da yan bindiga Gwamnan jihar Zamfara, Bello Muhammad Matawalle, a ranar Juma'a ya bayyana cewa sama da yan kasar waje 31 aka kora daga Najeriya saboda hakan ma'adinai ba bisa doka ba a jihar. Gwamna ya kara da cewa mutane 20 yan bindiga suka kashe ranar Laraba bayan rusa rundunar SARS da gwamnatin tarayya tayi, kisan-mutane-20-matawalle-ya-kaiwa-buhari-kuka-villa-hotuna. Gwamnat Matawalle ya bayyana hakan ne ga manema labaran fadar shugaban kasa bayan ganawa da shugaba Muhammadu Buhari inda ya bukaci a dawo masa da jami'an SARS. Ya kawo wa shugaba Buhari ziyara ne kan lamarin tsaron jihar. "Na zo ne domin bayyanawa shugaban kasa halin da jihar ke ciki. Bayan rusa rundunar SARS mun fuskanci wasu matsaloli, musamman shekaran jiya (Laraba) inda aka kashe mutane 20 a kar...
Comments
Post a Comment